28/06/2026
Idan Pantami Ya Zama Gwamnan Gombe, Ga kadan daga cikin Abubuwan Da za'a iya tsammani daga gare shi:
1. Gombe zata zama ta zamani, mai cike da fasahohin zamani (Smart Gombe): Pantami zai sauya Gombe zuwa jiha mai amfani da fasaha wajen gudanar da gwamnati, samar da ayyukan yi, da wayar da kan matasa. Matasa ba sai sun jira aikin gwamnati ba, zai koya musu yadda zasu ƙirƙiri nasu aikin na kansu.
2. Gwamnati mai gaskiya da rikon amana: A karkashinsa, dukiyar jihar Gombe zata kasance a sarari, kobo ɗaya ba zai ɓace ba. Kudin gwamnati zai shiga ayyuka, ba aljihu ba.
3. Amfani da arzikin man fetur na Kolmani: Pantami zai tabbatar da cewa man da aka gano a Gombe ya amfanar da talaka ta hanyar gine-gine, ayyukan yi, da kulawa da al’ummomin da ke kusa da rijiyoyin.
4. Inganta noma da tsaro ta hanyar fasaha: Zai kawo fasaha a noma da tsaro daga noma na zamani har zuwa amfani da drones don tsaron yankuna.
5. Koyar da matasa sana'o’in zamani: Zai bude cibiyoyin koyon ICT a ko'ina cikin jihar, inda matasa zasu rika samun horo kyauta kamar yadda yayi lokacin da yake Minista.
6. Gwamnatin zaman lafiya da adalci: Pantami zai yi shugabanci na kowa da kowa ba tare da wariya ba. Kowane yanki, addini ko kabila a Gombe zasu samu wakilci da kulawa (Kamar yadda addin mu ya koyar).
Professor Isa Ali Pantami ba dan siyasa kawai bane, Reformer ne. Ya tabbatar da hakan a matakin ƙasa. Yanzu kuma, yana shirye ya sake tabbatar da hakan a jiharsa ta Gombe, Gombe tana bukatar Gwamnan da aka gwada, aka yarda da shi, kuma ya dace da zamani.
Idan pantami ya zama gwamna canjin da zai kawo a Gombe ba daga Abuja bane zai kawo kamar lokacin da yake minista, daga cikin gombe ne, ku kwatanta abinda yayi a lokacin yana minista yana abuja, ina ga kuma ya dawo gida. Ba ayyuka a gabadaya nigeria zaiyi ba, a Gombe kadai.
Allah ya bashi nasara.
© Abdurrazak Saheel
Abba Sani Pantami
27/06/2026
Kamar yadda kuka gani duka mun yi ta amfani da bidiyon malam da muka saurara ne, amma shafin malam mai suna Professor Mansur Isa Yelwa sun ɗora bidiyon da rubutu a ƙasa (Matuƙar ba a gyara ba– na sauƙa daga limanci). Bayan bincike hakan ya tabbatar da cewa har yanzu malam bai sauƙa (officially) ba amma dai ya isar da gargaɗi mai ƙarfi sosai kuma saƙo ya isa har ya girgiza duk duniyar musulmi. Alhamdu LILLAH. ❤️
Yanzu dai ya rage wa hukumar makarantar A.T.B.U ta gaggauta yin abin da dukkanin musulmai suke so ta dakatar da ginin ƴan Tijjaniya a wannan makarantar saboda maslahar al'umma da wanzuwar haɗin-kai tsakanin ɗalibai. Hakan kuma shi zai sa V.C na yanzu ya fita daga zargin da tarihi zai na kallon shi da shi mai muni. 😢
Daga jiya zuwa yau kowa ya fahimci yadda wannan lamari ya sanya rabuwar kai tun kafin ma komai ya kankama, duka wannan alama ce ga jami'a ta duba kuma ta gaggauta janye wannan fili da ta ba wa Tijjaniya a A.T.B.U
Manufar Prof. Mansur Isa Yelwa shi ne zaman lafiya, domin duk duniya ba kowa ne zai iya sauƙa a matsayinsa ba domin zaman lafiya ya wanzu, domin ƙofar da za a buɗe za ta zama silar tarwatsa haɗin-kai da zaman lafiya na ɗalibai a wannan makaranta mai albarka shi ya sa Prof. ya fifita maslahar al'umma a kan tasa.
In kuma jami'a ta buɗe wannan ƙofa, Izala da Ƙadiriya da Shi'a da ƴan-tãtsine duka za su fito su gina nasu masallatan a cikin jami'ar, daga nan bãla'i ya fara, sai a dawo maganar bambanta lokutan sallah, shi ke nan sai a fara rigima daga ƙarshe faɗa tsakanin addinai ya tashi a jami'a wannan kowa ya san irin illar da hakan zai haifar mafi muni. SubhanALLAH. Allah tsare!
Babban kuskuren da Jami'a ta yi shi ne, fitar da takarda da sunan (Ɗaliban-Tijjaniya), amma da kawai gina masallaci aka yi sai aka yi dabaru aka ba wa ɗan Tijjaniya limanci da abin zai ɗan zo da sauƙi duk da haka sai an nemi shawarar babban liman saboda haka shugabanci ya tsara!
Amma lallai ayyana sunan wata Ƙungiya a inda akwai ƙungiyoyi masu yawa wannan haddasa fitina ne wanda ba a san ina ƙarshen wannan fitina zai tsaya ba! Kuma ba wai A.T.B.U kawai ba, tamkar ana zuga sauran Jami'o'i ne da su fito su ma su gina masallacinsu na daban... Sharrin hakan yana da illa mai girma ga dukkan mai tunani!
Alhamdu LILLAH. Ko yanzu duniya ta gane ƙarfi da tasirin Prof. Yelwa a duniya, ya rage wa Jami'a da V.C su tsare mutuncin tarihinsu a duniya da lahira, domin har ƙiyama Allah ba zai bar wanda ya yi sanadin tarwatsa haɗin-kai na bayin Allah musulmai ba. Innalillah wa'inna ilaihi rajiun! 😢
Allah muke roƙo ya ƙara tsare mana imaninmu, ya ba wa Jami'a ikon dakatar da wannan gini na Tijjaniya saboda maslahar al'umma da tsare mutuncin V.C daga mummunan tarihi.
Alƙalin bayan fage,
Ahmad Usman Elnafaty
26/06/2026
🚨 "Tinubu's administration is doing everything possible to prevent me from participating in the 2027 election."
— Peter Obi
26/06/2026
Ga hotunan Aliko Dangote, babban attajirin Afirka, a lokacin da yake gudanar da sallah tare da jama'a. Dangote sananne ne da halartar ibada da kuma ayyukan jin ƙai baya ga harkokin kasuwancinsa.
Dangote Industries
26/06/2026
Comr Aminu Abdussalam Gwarzo 🙌🙌