Jawabin Mai Girma Kwamishinan Ma’aikatar Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi ta Jihar Kano, Dr. Dahir Muhammad Hashim, yayin da ya kai ziyarar gani da ido zuwa matatun ruwa na Thomas da Ghari domin duba yadda ake gudanar da ayyukan samar da ruwa ga al’umma, tare da tantance matakan da ake ɗauka wajen tabbatar da samar da tsaftataccen ruwa ga jama’ar kauyukan jihar Kano.
VOK HAUSA
Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from VOK HAUSA, Sport & recreation, Gumel Road, Kano.
Ku kasance tare da Voice of Kano VOK HAUSA Domin Cigaba da samun Ingantattun Labarai Cikin Gaskiya da adalci
Ba San zuciya ba kazafi ko kage
Whatsapp no.090393935610. / 09035683171
28/06/2026
Kotu Ta Soke Rajistar NDC, Makomar Obi da Kwankwaso Ta Shiga Ruɗani
Wata kwafin hukuncin kotu (Certified True Copy) ta bayyana cewa Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta soke rajistar jam'iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC).
Alƙali Mai Shari'a Isa H. Dashen ya yanke cewa hukuncin da aka bayar a ranar 10 ga Disamba, 2025 wanda ya tilasta wa INEC ta yi wa NDC rajista ba zai ci gaba da aiki ba.
Kotun ta bayyana cewa an soke hukuncin ne saboda ya shafi haƙƙin jam'iyyar Peace Movement Party (PMP), wadda ta yi iƙirarin mallakar tambarin da NDC ke amfani da shi, alhali ba a saka ta cikin shari'ar tun farko ba.
Bayan wannan hukunci, ana sa ran INEC za ta cire NDC daga jerin jam'iyyun siyasa da ta amince da su.
Sai dai Kwamishinan INEC mai kula da yaɗa bayanai, Mohammed Kudu Haruna, ya ce har yanzu hukumar na jiran samun kwafin hukuncin kafin ta fitar da matsayarta a hukumance.
A wani sabon ci gaba kuma, NDC ta bayyana cewa har yanzu ba ta samu lambobin shiga tsarin INEC ba domin loda sunayen 'yan takararta na zaɓen 2027.
Wannan matsala na iya shafar shirye-shiryen siyasar Peter Obi, wanda aka tsayar takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin NDC, da kuma Rabiu Musa Kwankwaso, wanda aka zaɓa a matsayin mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa.
Kakakin NDC, Osa Director, ya tabbatar da cewa sun je INEC domin neman lambobin shiga tsarin, amma an ce musu za a sake tuntubarsu.
Ya kuma bayyana cewa jam'iyyar na shirin komawa kotu domin neman dakatar da aiwatar da hukuncin.
Kalli Yadda Commissioner ya Kai ziyara ma'aikatar Ruwa ta Wudil
24/06/2026
Dr. Bello Matawalle ya ƙaddamar da tafiyar “Tinubu Again” a hukumance, wani sabon yunƙuri na ƙasa baki ɗaya da aka kafa domin nuna goyon baya ga Shugaban Ƙasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.
An gina wannan shiri ne bisa ƙwarin gwiwar cewa manufofi da tsare-tsaren da gwamnatin ke aiwatarwa a halin yanzu suna shimfiɗa tubalin samar da Najeriya mai tsaro da wadata.
Ta hanyar ƙaddamar da wannan tafiya, Matawalle na da burin haɗa kan al’ummar Najeriya daga kowane yanki na ƙasar da ke son ganin an cika manufar “Renewed Hope” ta Shugaba Tinubu. Wannan dandali zai zama cibiyar haɗin kai ga ‘yan ƙasa, ƙungiyoyin al’umma da sauran ƙungiyoyi domin mara wa hangen nesan Shugaban Ƙasa baya, tare da ƙarfafa yunƙurin sake zaɓensa a shekarar 2027.
A ƙarshe, wannan kira ne ga duk masu imani da alkiblar gwamnatin da ke kan mulki da su haɗa kai domin tabbatar da cewa manufofin ci gaban ƙasa sun ci gaba da gudana zuwa nan gaba.
DAVIDO YAYI WA RARARA MARTANI CIKIN SABUWAR WAKAR SA.
SAURARA KAJI
16/06/2026
Kotun daukaka kara dake zamanta a birnin tarayya Abuja ta bayar da umarnin jingine hukuncin kotun tarayya kan soke rijistar Jam’iyyun siyasa hudu ciki da jam’iyyar adawa ta ADC.
Hukuncin kotun tarayyar da yamutsa hazo a kasar wanda ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta tabbatar da ta soke rijistar jam’iyyun, sai dai kotun daukaka kara ta ce kada a aiwatar da hukunci.
A cikin wani hukunci na haɗin gwiwa, kwamitin alkalai uku na Kotun Ɗaukaka Ƙara, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Abubakar Mohammed, ya zargi Alkalin babbar Kotun tarayyar da ke Abuja, Mai Shari’a Peter Lifu, da saba wa umarnin da kotun ta bayar a ranar 22 ga watan Mayu.
Wannan umarni na baya dai ya umarci Mai Shari'a Lifu ne da ya dakatar da duk wata shari'a ko gudanar da bincike a kan shari'ar da ke gaban shi har sai an kammala nazari.
16/06/2026
11/06/2026
Gwamnatin Nijeriya ta ayyana Juma’a a matsayin ranar hutun ranar Dimokuraɗiyya
Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Juma’a 12, ga watan Yunin 2026, a matsayin ranar hutu ga ma’aikata da sauran al’umma domin bikin cika shekaru 27 da komawar ƙasar kan mulkin dimokuraɗiyya.
A wata sanarwa da babbar Sakatariyar a ma’aikatar harkokin cikin gida, Magdalene Ajani, ta fitar ta cewa hutun na daga cikin bukukuwan ranar Dimokuraɗiyya ta ƙasa.
Gwamnatin ta ce bikin na bana wata dama ce ta tunawa da irin gudunmawar da magabata da sauran masu fafutukar dimokuraɗiyya s**a bayar wajen tabbatar da mulkin farar hula a Nijeriya.
11/06/2026
INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!!
Duniya Ba Tabbas
Wannan wani matashi ne ɗan Acaba a Portharcourt da aka ce barayin mashin sun kashe shi.
Tsawon sati 3 ana ta neman sa cikin damuwa da fatan za a gan shi da rai, amma abin takaici sai yau aka gano gawar sa bayan ta lalace sosai. 😭
Wallahi rayuwa ba ta da tabbas. Mutum na fita neman abincin iyalinsa da safe, amma ba kowa ne yake dawowa gida da yamma ba.
Allah Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya ba iyalansa haƙurin jure wannan babban rashi.
DARASI: Mu yawaita tuba, mu gyara alakar mu da Allah, domin ba mu san ranar da za a kira sunan mu ba.
- Maryam Dosty
08/06/2026
Kada a ɗora laifin masu aikata laifi kan daukacin Fulani - Obi
Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su daina danganta laifuffuka da wata ƙabila, yana mai cewa hakan na haifar da ƙiyayya tare da barazana ga haɗin kan ƙasa.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, Obi ya ce mutane da dama a Najeriya sun sha fuskantar wariya da tsangwama saboda asalinsu na ƙabila.
Ya bayyana cewa a matsayinsa na ɗan kabilar Igbo, ya sha fuskantar hukunci da lakabi saboda ƙabilarsa, yana mai cewa irin wannan matsala ba ta Igbo kaɗai ba ce, domin yawancin ‘yan Najeriya sun taɓa fuskantar hakan.
Obi ya ce yana fahimtar halin da talakawan Fulani ke ciki, inda ake yawan kallon su a matsayin masu laifi saboda ayyukan wasu ‘yan ta’adda da masu aikata laifuffuka da ba su da alaƙa da su.
Ya jaddada cewa laifi ba shi da ƙabila, yana mai cewa barawo barawo ne, ɗan ta’adda ɗan ta’adda ne, sannan mai garkuwa da mutane ma mai laifi ne, ba wakilin wata ƙabila ba.
Tsohon gwamnan jihar Anambra ya buƙaci hukumomi su riƙa k**a tare da gurfanar da masu laifi gaban kuliya bisa doka, maimakon ɗora laifinsu kan daukacin wata ƙabila.
Obi ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su rungumi bambancin al’adu da ke cikin ƙasar tare da gujewa son zuciya da ra’ayoyin wariya da wasu ‘yan siyasa ke amfani da su domin cimma muradunsu.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Website
Address
Kano