24/06/2026
Da yake zantawa da manema labarai, Shugaban Kwamitin Kar-ta-Kwana na Dakile Gine-ginen da Ba Su Cika Ka’idoji ba, kuma Shugaban Riƙo na Hukumar Tsara Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Dakta Dalhatu Aliyu Sani, ya bayyana hakan ne jim kaɗan bayan rufe ginin.
Ya ce za a ci gaba da kulle wurin har sai gwamnatin jihar ta kammala bincike da nazarin lamarin, domin ɗaukar matakin da ya dace bisa sakamakon binciken.
24/06/2026
"Da na yi tafiya da Rarara wallahi ni Iyantama, gara na mutu, ni uban Rarara ne a siyasa. Ni ne na kai shi Buhari Organization, kuma bana APC a matsayin na dan Kannywood"
- Hamisu Lamido Iyantama
24/06/2026
Sanusi Bature Dawakin Tofa ya bayyana Kwamared Aminu Gwarzo a matsayin ɗan siyasa mai rowa kuma mai rauni wajen taimakawa al'umma.
Sanusi Bature ya kuma bayyana jin daɗinsa da Aminu Gwarzo ya kira kansa da tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Kano.
A cewarsa:
“A duk faɗin Jihar Kano, babu mutum guda da za a iya nunawa a ce Comrade Aminu Gwarzo ya taɓa taimaka masa da kuɗi har naira miliyan ɗaya.”
Me za ku ce kan wannan zargi?
24/06/2026
Malam Ali Bichi ya bayyana dalili da ya sa har yanzu gwamnatin Abba Kabir Yusuf bata cire Jar hula ba ta Kwankwasiyya.
Inda Yace:
"Kwankwasiyya Amana tana Hannun Gwamna Abba Kabir Yusuf shiyasa ba’a cire Jar hula ba, Kwankwasiyya Gantaliyya tana wajan su Sunusi Surajo."
–Malam Ali Muhammad Bichi
Me za ku ce?
24/06/2026
"Sanusi Bature D-Tofa Yace Duk faɗin kano babu wani mutum ɗaya da kwamared Aminu gwarzo ya taba taimakawa da kuɗi naira miliyan daya"
24/06/2026
Da ɗumi-ɗumi: 'Yan bindiga sun yi garkuwa da mata da ɗan Shugaban Jam'iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Yauri, Alhaji Yusuf Alhasan, a Jihar Kebbi.
Rahotanni daga garin Yauri sun nuna cewa maharan sun kai harin ne a gidansa da ke Unguwar Low-Cost da tsakar daren Lahadi zuwa safiyar Litinin, inda s**a yi awon gaba da matar da ɗansa.
Har zuwa yanzu ba a san inda masu garkuwar s**a tafi da su ba, yayin da hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.
23/06/2026
Cikin Hotuna: Yadda Tawagar Shugaban Kasa Ta Gabatar Da Ta'aziyya Ga Farfesa Pakistan.
Mai Girma Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya aiko da wata babbar tawaga karkashin jagorancin Babban Mai Taimaka Masa na Musamman, H.E. Ibrahim Kabir Masari.
Sauran membobin tawagar sun hada da Ministan Gidaje da Raya Birane, Engr. Muttaqha Rabe Darma; Shugaban Hukumar Ilimin Almajirai, Dr. Muhammad Sani Idris; da kuma Jami'in Gudanarwa na Hukumar NEPAD na Kasa, Malam Jabiri Salisu Abdullahi. Sun zo ne domin su mika ta'aziyya ta musamman ga Farfesa Abdullahi Sale Pakistan, bisa ga rasuwar matarsa.
A jawabin Shugaban Kasa da Babban Mai Taimaka Masa kan Harkokin Siyasa da Sauran Al'amura, H.E. Ibrahim Kabir Masari, ya gabatar, ya bayyana cewa: "Mai Girma Shugaban Kasa ya turo mu ne domin mu jajantawa daukacin al'ummar Jihar Kano, ba wai Farfesa Pakistan kadai ba, tare da yi wa marigayiyar addu'a ta musamman."
Yayin wannan ziyara, tawagar shugaban kasa ta samu kyakkyawar tarba daga manyan malamanmu na Jihar Kano, da masu ruke sarauta, da sauran masoya.
An kammala ziyarar ta'aziyyar da yi wa kasa addu'ar Allah ya ba mu lafiya da zaman lafiya, kuma ya magance mana abubuwan da s**a fi karfinmu.
Muna addu'ar Allah ya mayar da wannan tawagar gida cikin koshin lafiya, ya ba su nasara a dukkan al'amuransu. Allah ya ba kasarmu lafiya da zaman lafiya, ya kuma yi mana maganin duk abin da ya fi karfinmu. Amin.
23/06/2026
“Babu wanda na ke ji a jiki na tun kafin ya mutu, Aljanna ta na jiransa kamar Bola Tinubu.”
~Dauda Kahutu Rarara.